Monday, 7 December 2015

Za a karawa sojoji wa'adin murkushe Boko Haram

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana aniyarsa ta karawa sojojin kasar wa'adin da ya dibar musu na murkushe kungiyar Boko Haram.
A kwanakin baya ne dai shugaban ya bai wa sojojin umarnin kawar da kungiyar kafin karshen watan Disambar da muke ciki.
Sai dai a wani taron manyan jami'an rundunar sojin kasar da aka yi a birnin Dutse na jihar Jigawa, Babban Hafsan tsaron Najeriya, Janar Abayomi Gabriel Olonishakin, wanda ya karanta jawabin Shugaba Buhari, ya ambato shi yana cewa a shirye gwamnatinsa take ta kara wa sojojin wa'adi idan suka bukaci hakan.

TALLA

Kungiyar ta Boko haram dai ta kashe dubban mutane, sannan ta kori miliyoyin mutane daga gidajensu, musamman a jihohin Borno da Yobe da Adamawa.

Blogger
Disqus
Pilih Sistem Komentar Yang Anda Sukai

No comments

Disclaimer: Opinions expressed in comments are those of the comment 💬📝writers alone and does not reflect or represent the views of CLICKNAIJ Blog🚯