Showing posts with label Labaran hausa. Show all posts
Showing posts with label Labaran hausa. Show all posts

Wednesday, 18 October 2017

Sunayen kwamishinonin da Ganduje ya kora da sabbin da aka nada

Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya kori wasu kwamishinonin sa biyar inda ya nada wasu a madadin su.

Wadanda aka sallama sune, Kabiru Dandago, Hamisu Lambu, Rabiu Bako, Zubaida Damakka da Haruna Falali.

Sabbin da aka nada kuma sune Ibrahim Muhammad, five others, Aminu Aliyu, Aminu Dan Amu, Musa Kwankwaso, Ahmed Rabiu da Aisha Jaafar.

Gwamnan ya gode wa wadanda aka sallama cewa za a iya nada su wasu mukaman idan ana bukatan hakan.

Wednesday, 6 September 2017

YADDA SAMA DA MUSULMAI DUBU TALATIN SUKAYI HIJIRA CIKIN KANKANIN LOKACI DAGA BURMA



DAGA AUWAL M KURA
Kasa da awanni ashirin da hudu al-ummar Rohingya kusan Dubu Talatin da bakwai (37,000) suka tsere zuwa Bangladesh
Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla musulmai ‘yan
Kabilar Rohingya dubu talatin da Bakwai ne, (37,000) suka tsere zuwa kasar Bangladesh cikin Awanni ashirin da hudu24 bayan irin kisar girlar da akeyi musu a kasar Burma
Inda majalisar dinkin duniya ta Bayyana  lamarin da matsayin Gudun hijira mafi girma da aka Taba gani cikin karamin lokaci Tun bayan sabon tashin Hankalin da ya barke a kasar Myanmar .
A cewar Majalisar, wannan ta sa Yawan ‘yan kabilar Rohingya da suka tsere daga  burma zuwa Bangladesh ya karu zuwa dubu Dari da ashirin da biyar (125,000) daga dubu Casa’in (90,000)

A Karo Na Biyu Buhari Ya Soke Zaman Majalisar Ministoci



A karo na biyu tun bayan da ya dawo jinya daga waje, Shugaba Muhammad Buhari ya soke zaman majalisar ministoci wanda aka tsara gudanarwa a yau Laraba.
Ministan Yada Labarai, Lai Mohammed ya ce an soke zaman majalisar ce saboda rashin isasshen lokaci da ministocin za su nazari kan batutuwan da aka tsara tattaunawa a lokacin zaman sakamakon bukukuwan Babban sallah da aka gudanar.

2019: Ministar Harkokin Mata Ta Fara Yi Wa Atiku Kamfe


Ministar harkokin mata, Hajiya Aishatu Isma'ila ta soma yi wa tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar yakin neman zabe na shekarar 2019. Ministar, wacce ta jagoranci shugabannin jam'iyyar APC na jihar Taraba domin kai gaisuwar Sallah ga Atiku Abubakar, ta yi addu'ar Allah ya ba shi shugabancin kasar a 2019.

Wani bidiyo da jaridar Daily Nigerian wacce ake wallafawa a shafin intanet ta buga, ya nuna ministar a gaban tsohon mataimakin shugaban kasar tana cewa, "Your Excellency (mai girma), babanmu, shugaban kasarmu idan Allah ya yarda a shekarar 2019... a gabanka, mutanenka ne, magoya bayanka har abada; mutanen jihar Taraba.

"Sun zo gaisuwar ban-girma, gaisuwar Sallah da kuma yi maka murna ta wannan daukaka (Wazirin Adamawa) da Allah ya kara  Minista Alhassan ya gabatarwa tsohon mataimakin shugaban kasar shugabannin jam'iyyar, tana mai cewa wasunsu sun matsa domin su yi jawabi a gabansa amma hakan ba zai yiwu ba saboda ya gaji.

Tawagar ta rika yin tafi a lokacin da ministar ke wadannan jawabai.
Ministar ta harkokin mata dai ita ce ta yi takarar gwamnan jihar Taraba a karkashin jam'iyyar APC a shekarar 2015, ko da yake ta sha kaye a hannun Gwamna mai-ci, Darius Ishaku na jam'iyyar PDP.

Saturday, 30 January 2016

Dakarun Turai sun yi lalata da yara a CAR'

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta bankado karin lalatar da dakarun Turai suka yi da yara a Jamhuriyyar Afrika ta Tsakiya.
Babban jami'in kare hakkin bil Adama na Majalisar Zeid Ra'ad Al Hussein, ya ce an yi lalata da yaran ne a kusa da wani sansanin 'yan gudun hijira da ke filin jiragen sama na Bangui.
Masu bincike na Majalisar sun ce wata yarinya 'yar shekara bakwai ta shaida musu cewa, sojojin Faransa sun yi lalata da ita kafin a bata ruwa da biskit.
Mista Zeid ya ce lamarin ya faru ne a shekarar 2014, amma bai fito fili ba sai a 'yan makonnin nan.

Sunday, 13 December 2015

Mugabe ya yi katobara

Shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe ya sake yin wata kwaba, inda ya karanta wani jawabin da ba shi da alaka da wani taron ya halarta.
Shugaba Mugabe ya karanta jawabin ne a wajen taron shekara-shekara na jam'iyyar Zanu-PF mai mulkin kasar, kuma sai da ya ci kusan rabin minti yana karanta jawabin kana aka sauya masa da jawabin da ya dace da taron.
A watan Satumban da ya wuce ma, shugaba Mugaben ya karanta wani tsohon jawabi a majalisar dokokin kasar, wanda ya taba karantawa a baya, kimanin wata guda.
TALLA

A jawabinsa na taron jam'iyyar Zanu-PF din, Mista Mugabe ya bukaci 'ya'yan jam'iyyar da su daina fada su-ya-su a kan wanda zai gaje shi wajen mulkin kasar ta Zimbabwe.

Monday, 7 December 2015

Za a karawa sojoji wa'adin murkushe Boko Haram

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana aniyarsa ta karawa sojojin kasar wa'adin da ya dibar musu na murkushe kungiyar Boko Haram.
A kwanakin baya ne dai shugaban ya bai wa sojojin umarnin kawar da kungiyar kafin karshen watan Disambar da muke ciki.
Sai dai a wani taron manyan jami'an rundunar sojin kasar da aka yi a birnin Dutse na jihar Jigawa, Babban Hafsan tsaron Najeriya, Janar Abayomi Gabriel Olonishakin, wanda ya karanta jawabin Shugaba Buhari, ya ambato shi yana cewa a shirye gwamnatinsa take ta kara wa sojojin wa'adi idan suka bukaci hakan.
TALLA

Kungiyar ta Boko haram dai ta kashe dubban mutane, sannan ta kori miliyoyin mutane daga gidajensu, musamman a jihohin Borno da Yobe da Adamawa.

Lafiyata kalau - Adam A. Zango

Jarumin fina finan nan Hausa Adam A Zango ya ce lafiyarsa kalau sabanin jita-jitar da ake yadawa cewa an yi mi shi duka.
Jarumin ya karyata jita-jitar da ake yadawa a dandalin sada zumunta na intanet a inda ake yada labarin cewa barayi sun jikkata shi a sakamakon dukan da suka yi masa.
Shahararren mawakin ya kara da cewa hotunan da ake yadawa da raunuka a jikinsa na fim din Basaja ne wanda ake yi masa kwalliya, ba raunin gaske ba ne. Ya kuma yi kira ga masu kirkirar irin wadannan karai rayi da su daina.

Abinda Burtaniya ta ke bai dace ba_ Assad

Shugaba Bashar Al-assad ya kira matakin da Burtaniya ta dauka na kai hare-hare ta sama cikin Syria da haramtacce ne. Ya yi wannan jawabi ne a wata hira da ya yi da gidan jaridar Sunday Times ta Burtaniya

Saturday, 5 December 2015

An gano inda ‘Yan Boko Haram ke kulle-kullen kai hari a Abuja

Yan Boko haram sun sha kai hare hare a Abuja birnin Tarayyar Najeriya REUTERS




Jami’an tsaron farin kaya a Najeriya sun ce sun gano wani wurin da mayakan Boko haram ke shirin kulla kai hare hare a babban birnin Tarayya Abuja. wannan kuma na zuwa ne a yayin Ofishin jekadancin Amurka ya yi gargadin cewa ana shirin kaddamar da hare haren ta’addanci a wasu wuraren da Turawa ke sauka.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar tace, sun samu haske ne daga wadanda aka kama da suka gudo daga yankin arewa maso gabashin Najeriya zuwa Abuja kan inda ake kulla kai hare-haren.

A cikin sanarwar hukumar ta zayyana sunayen ‘yan Boko haram da ta kame a Abuja wadanda suka jagoranci kai hare-hare a Jihohin Yobe da Filato da Kano da kuma Kaduna.
Ofishin jekadancin Amurka a Najeriya yace ya samu labarin ana shirin kai hare-haren ta’addanci a wasu mayan wuraren da ‘Yan kasashen waje ke sauka, sai dai ba tare da bayyana lokacin da za a kai hare-haren ba.

Ofishin jekadancin ya gargadi Amurkawa su yi taka-tsantsan a wuraren da suka sauka.

A watan jiya kimanin mutane 20 aka kashe a wata babbanr Otel a birnin Bamako na kasar Mali, Inda yawanci Turawa ke sauka.